GIDAN MARIGAYI DAN KABO KANO ZAI FARFADO_SARKIN KANO

GIDAN MARIGAYI DAN KABO KANO ZAI FARFADO
Mai Martaba Sarkin Kano Khalifa Dr. Muhammad Sanusi II, CON, PhD, zai farfaÉ—o da gidan Marigayi Jarman Kano Alhaji Muhammad Adamu Dankabo, Mai Kamfanin Jirgin sama na Kabo Air.

A wata sanarwa da sakataren Masarautar Kano Danmakwayon Kano Alhaji Abba Yusuf ya fitar, Sarkin Kano Khalifa Sanusi II zai nada Babban Dan Marigayin Alhaji Idris Muhammad Adamu Dankabo a matsayin Sarkin Gabas din Kano Hakimin Kabo. Nadin Wanda za’ayi ranar jumu’a 27 ga watan disambar da mukeciki na shekarar 2024 za’ayi shi ne a fadar Masarautar Kano dake gidan Rumfa da karfe 9 na safe.

Wannan yana cikin Æ™udurin Mai Martaba Sarki na farfaÉ—o da gidaje muhimman mutane a Kano da aka manta da su, dan cigaba da karfafar zumunci da adalci tsakanin Al’ummah.

Kuci gaba da bibiyarmu domin samun wasu sabbin labarai


Post a Comment

0 Comments